fidelitybank

Argentina ta gayyaci Messi ya buga mata wasanni biyu

Date:

Lionel Messi na shirin buga wa tawagar Argentina tamaula a karon farko, tun bayan lashe kofin duniya a Qatar a 2022.

Argentina ta samu daukar kofin duniya na uku jimilla, bayan da ta yi nasara a kan Faransa a bugun fenariti a wasan karshe.

Koci, Lionel Scaloni ya gayyaci ‘yan wasa 35, domin buga wa Argentina wasan sada zumunta, cikinsu har da dukkan 26 da suka buga kofin duniya a Qatar.

An gayyaci Giovanni Lo Celso, wanda rauni ya hana shi zuwa Qatar da dan wasan Manchester United Alejandro Garnacho, wanda karon farko aka bashi goron gayyata.

An kuma kira wasu ‘yan kwallon a karon farko da ya hada da dan wasan Manchester City, Maximo Perrone da Facundo Buonanotte na Brighton da dan kwallon Inter Milan, Valentin Carboni.

Argentina za ta karbi bakuncin Panama ranar 23 ga watan Maris Buenos Aires asannan ta kece raini da Curacao a Santiago del Estero kwana biyar tsakani.

An yi ta rade-radin cewar Messi zai yi ritaya, bayan da dan wasan mai shekara 35 ya ja ragamar tawagar ta lashe kofin duniya a Qatar.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp