Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ta ce, Arewa za ta biya dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu sakamakon goyon bayan da ta bai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Aminu Jaji, Daraktan tuntuba da wayar da kan jama’a na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa (PCC) na yankin Arewa maso Yamma, ya yi magana a ranar Alhamis.
A wajen kaddamar da kwamitin a Abuja, Jaji ya ce kuri’un da za su fito daga yankin Arewa maso Yamma ne za su tabbatar da wanda zai shugabanci kasar nan.
Basaraken ya bayyana kwarin gwiwar cewa tsohon gwamnan Legas zai zama shugaban kasa a 2023.
Dangane da sakamakon zabukan 2015 da 2019, Jaji ya yi imanin APC za ta kai ga nasara saboda farin jininta.
“Mafi kyawun abin da za mu iya yi shi ne mu mayar wa Tinubu wanda ya goyi bayan danmu, Shugaba Buhari ya zama shugaban kasa sau biyu.
“Lokaci ya yi da za mu biya abin da sauran shiyyar suka yi wa ɗanmu; uba kuma abin koyi, Shugaba Buhari,” NAN ta ruwaito yana cewa.
Jaji ya ba da tabbacin cewa za a mara wa Tinubu baya ba tare da wani sharadi ba, amma ya kamata ya ba da tabbacin ci gaban Arewa.