fidelitybank

Arewa maso Yamma su ne a kan gaba wajen yin rijistar zabe a bana – INEC

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana cewa shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu-maso-Yamma ne ke kan gaba wajen rajistar masu kada kuri’a da 22,672,373 da 18,332,191.

Wani sabon rahoto da aka buga a yanar gizo na INEC ya nuna cewa, mutane 96,303,016 ne suka yi rajista kafin a dakatar da rajistar masu zabe a ranar 31 ga watan Yuli.

A shekarar 2019, hukumar ta yiwa masu jefa kuri’a 84,004,084 rajista. Alkaluman da hukumar zabe ta INEC ta fitar a shekarar 2022 sun nuna an samu karuwar masu rajista da yawansu ya kai 12,298,932 gabanin babban zaben shekarar 2023.

Arewa-maso-Yamma, wadda ta kunshi jihohi bakwai (Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sokoto da Zamfara), nada masu zabe 22,672,373. Yankin Kudu-maso-Yamma da ya kunshi Legas, Oyo, Ondo, Osun da Ekiti sun bi sahun masu kada kuri’a 18,332,191.

Arewa ta tsakiya ta zo na uku da 15,680,438 da suka yi rajista, dan sama da Kudu maso Kudu da 15,299,374. Yankin Arewa-maso-Gabas na da masu jefa kuri’a 12,820,363 ya zuwa yanzu. Kudu-maso-Gabas na da mutane 11,498,277 da suka cancanci kada kuri’a.

Bayanai na INEC sun kara nuna cewa sama da kashi 50 cikin 100 (8,854,566) na sabbin masu kada kuri’a 12,013,068 ne suka yi rajista da kansu, wasu kuma (3,444,378) sun yi rajista ta yanar gizo.

Hakanan, sama da sabbin masu jefa ƙuri’a miliyan 12 sun ƙunshi maza 6,074,078 da mata 6,224,866.

KARANTA WANNAN: INEC ta yi gargaɗi a kan shafin rijistar zabe na bogi

Duk da cewa, kungiyoyin kare hakkin jama’a da jam’iyyar All Progressives Congress mai mulki sun yi yunkurin tsawaita rajistar masu kada kuri’a (CVR), INEC ta dakatar da yin rajistar ne bayan wa’adin ranar 31 ga watan Yuli.

Tun da farko dai INEC ta kara tsawaita rajistar CVR daga ranar 30 ga watan Yuni zuwa 31 ga watan Yuli.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp