fidelitybank

Aregbbesola ya goge sakon da ya wallafa a kan Tinubu bayan cece-kuce da aka yi

Date:

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya goge wani rubutu mai cike da cece-kuce a shafinsa na Facebook, inda ya bayyana farin cikinsa kan kayar da gwamna mai ci kuma dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Gboyega Oyetola, da dan takarar jam’iyyar PDP, Ademola Adeleke ya yi a Jam’iyyar (PDP).

A wani sako da ya wallafa a Facebook ranar Lahadi, Aregbesola ya tabbatar da nasarar da Ademola Adeleke ya samu a kan Oyetola mai ci, ta hanyar sanya wata ayar Littafi Mai Tsarki.

Ya dai wallafa sakon ne da misalin karfe 8 na safe, bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta tabbatar da Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben kuma zababben gwamna.

Wannan magana dai ta yi kaca-kaca da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu, domin ya nuna cewa Allah ya fi shi iko.

Ana zargin ministan ya dauki nauyin Alhaji Moshood Adeoti, tsohon sakataren gwamnati ne domin ya fafata da Oyetola a zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Bayan nasarar Oyetola, Adeoti ya maka Oyetola kotu, inda ya nemi a soke shi, saboda rashin yin murabus da wuri daga kwamitin rikon jam’iyyar na kasa.

Yayin da kotu ta yi watsi da karar a ranar Alhamis, rahotanni sun ce Aregbesola ya bar kasar zuwa Amurka, inda ya nuna ba zai halarci zaben gwamnan Osun ba.

To sai dai bayan da aka yi ta cece-kuce kan rubutun da aka yi a Facebook, Aregbesola ya goge shi.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...

Najeriya ba za ta karbi ‘yan ciranin Venezuela ba da Amurka za ta ba mu – Najeriya

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ce ƙasar...

Bafarawa ya kafa sabuwar kungiya

Wasu shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki daga...

An fara shirye-shiryen aikin Hajjin badi a Najeriya

Hukumar Alhazan Najeriya ta fara shirhin aikin hajjin 2026...

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne...

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Ministar al'adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya...

Rashin abinci mai gina jiki Najeriya ce kan gaba a Afirka ta biyu a duniya

Babbar mai taimaka wa shugaban Najeriya Bola Tinubu kan...
X whatsapp