Jam’iyyar All Progressives Grand Alliance (APGA) a jihar Ebonyi ta tsayar da ranar 12 ga watan Yuli, domin gudanar da wani zagaye na zaben fidda gwani, domin maye gurbin ‘yan takarar da suka fice daga jam’iyyar gabanin babban zaben 2023.
Shugaban jam’iyyar APGA a Ebonyi, Ricky Okorouka, ya bayyana a ranar Lahadi a Abakaliki cewa, ‘yan takara za su fafata a zaben ‘yan majalisar dattawa da na wakilai da dai sauransu.
“Za a gudanar da zaben ne a sakatarorin jam’iyyar da ke jihar. Mun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta sanya ido a kan aikin,” inji shi.
Mista Okorouka ya bukaci ’yan uwa da su tsaya tsayin daka da kuma kiyaye ka’idoji da akidun jam’iyyar.
“Muna da niyyar maimaita irin kwarewar da Anambra ta samu a Ebonyi bayan zaben fitaccen dan takara a zaben gwamna a 2023,” in ji shi.