Jagoran jam’iyyar APC na kasa, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar da cewa, jam’iyyar za ta ci gaba da kasancewa a dunkule bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa.
Asiwaju Tinubu, wanda tsohon gwamnan jihar Legas ne kuma ya ce, karuwar masu neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar abu ne mai kyau ga dimokuradiyya.
Shugaban jam’iyyar APC na kasa ya bayyana haka ne da yammacin jiya Talata bayan ganawarsa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
An tattaro cewa Tinubu, ya gana da shugaba Buhari a fadar sa da ke Villa, domin yi masa gaisuwar Sallah ta gargajiya.