Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar APC na kasa, Yekini Nabena, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta girgiza gwamna mai ci Duoye Diri da jam’iyyar PDP mai mulki a ranar zabe.
Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, a ranar Juma’a ya kaddamar da kungiyar yakin neman zabe na kasa da wani aiki na hada kai, nazarin dukkan ka’idoji da kuma isar da dan takarar jam’iyyar, Timipre Sylva.
Da yake magana da manema labarai, Lahadi a Abuja, Nabena ya kalubalanci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, da ta gaggauta bayyana ka’idojin zaben da za ta yi amfani da su a fili domin gudun rudani.
Ya ci gaba da cewa INEC tana da hakkin fadawa masu kada kuri’a ko za ta yi amfani da BVAS da kuma ko za ta mika sakamakon zabe daga sashin zabe.
Nabena ya bayyana cewa: “Na farko dai ya kamata a maida hankali kan tsarin tsaro a jihar Bayelsa. Kuma yakamata INEC ta fito karara a wannan karon. Shin BVAS ne ko kuwa muna yin duk abin da muke so mu yi yayin da INEC ta dauke ta daga can? Babu bayyanannen alkibla. Don haka za ku iya yin duk abin da kuke so ku yi to INEC za ta iya dawowa ta yi abin da ta ga dama. Suna gaya mana INEC ta ce ba su da ikon watsawa.
“Dole ne INEC ta samu kyakkyawar alkibla domin masu kada kuri’a su san wannan shi ne tsarin. Domin kowa ya kare kuri’arsa. Ba wai wanda zai je gidan gwamnati ya rubuta wa INEC wadannan abubuwa ba.
“Don haka gaya mana, za ku watsa sakamakon daga rumfunan zabe? Ko me za ku yi? Shin za ku yi amfani da BVAS? Fada mana daga rana ta daya. Bari a sami jagora da fahimtar cewa wannan shine. Ba kotu daya ce za ta ce INEC za ta iya kawo duk wani abin da suke so ba. Siyasa ita ce babbar kasuwanci a duniya.”
Da aka tambaye shi game da damar jam’iyyar a zabe mai zuwa, Nabena haifaffen Bayelsa ya kara da cewa: “Za mu yi nasara. Mun yi shi a baya, za mu sake yi.