Jam’iyyar APC ta saka ranar Talata 25 ga watan Fabrairu da Laraba, 26 ga Fabrairu domin gudanar da taron masu ruwa da tsaki, da kuma babban taronta.
Sakataren jam’iyyar na Ć™asa, Surajuddeen Bashiru ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a a Abuja.
Sanarwar ta ce za a yi taron masu ruwa da tsakin a daĆ™in taro na Banquet da fadar shugaban Ć™asar Najeriya, sannan a gudanar da babban taron jam’iyyar a ranar Laraba a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja.