fidelitybank

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi nasarar lashe zaɓen cike gurbi na ɗanmajalisar tarayya da aka gudanar a jiya Asabar, kamar yadda hukumar zaɓe ta bayyana.

Baturen zaɓe Fafesa Salisu Ibrahim ya ce Rabiu Mukhtar na APC ne ya lashe zaɓen na mazaɓar Garki-Babura da ƙuri’a 38,449.

A cewar baturen zaɓen, ɗantakarar jam’iyyar PDP Auwalu Isa ne ya zo na biyu bayan ya samu ƙuri’a 13,519.

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta lashe duka zaɓukan cike gurbi uku da aka gudanar a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar, kamar yadda hukumar zaɓe ta Inec ta sanar.

Sakamakon da aka gudanar a mazaɓar majalisar tarayya ta Chikun/Kajuru ya nuna cewa Felix Bagudu na APC ɗin ya samu ƙuri’a 34,580 kuma ya doke na PDP da ya zo na biyu da ƙuri’a 11,491.

Kazalika, APC ta yi nasarar cin zaɓen ‘yanmajalisar jiha na mazaɓun Zaria/Kewaye da kuma Basawa.

Baturen zaɓe na Zaria Kewaye Balarabe Abdullahi ya sanar cewa ɗantakarar APC Haruna Ihamo ne ya cinye da ƙuri’a 26,613, yayin da abokin hamayya na SDP Nuhu Sada ya samu 5,721.

A zaɓen Basawa kuma, baturen zaɓe Farfesa Nasiru Rabiu ya ce APC ta samu ƙuri’a 10,926 kuma ta doke PDP mai 5,499.

Da ma APC ce ke mulkin jihar ta Kaduna bayan ɗantakararta Uba Sani ya lashe zaɓen gwamna na watan Maris ɗin 2023.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp