fidelitybank

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi nasarar lashe zaɓen cike gurbi na ɗanmajalisar tarayya da aka gudanar a jiya Asabar, kamar yadda hukumar zaɓe ta bayyana.

Baturen zaɓe Fafesa Salisu Ibrahim ya ce Rabiu Mukhtar na APC ne ya lashe zaɓen na mazaɓar Garki-Babura da ƙuri’a 38,449.

A cewar baturen zaɓen, ɗantakarar jam’iyyar PDP Auwalu Isa ne ya zo na biyu bayan ya samu ƙuri’a 13,519.

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta lashe duka zaɓukan cike gurbi uku da aka gudanar a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar, kamar yadda hukumar zaɓe ta Inec ta sanar.

Sakamakon da aka gudanar a mazaɓar majalisar tarayya ta Chikun/Kajuru ya nuna cewa Felix Bagudu na APC ɗin ya samu ƙuri’a 34,580 kuma ya doke na PDP da ya zo na biyu da ƙuri’a 11,491.

Kazalika, APC ta yi nasarar cin zaɓen ‘yanmajalisar jiha na mazaɓun Zaria/Kewaye da kuma Basawa.

Baturen zaɓe na Zaria Kewaye Balarabe Abdullahi ya sanar cewa ɗantakarar APC Haruna Ihamo ne ya cinye da ƙuri’a 26,613, yayin da abokin hamayya na SDP Nuhu Sada ya samu 5,721.

A zaɓen Basawa kuma, baturen zaɓe Farfesa Nasiru Rabiu ya ce APC ta samu ƙuri’a 10,926 kuma ta doke PDP mai 5,499.

Da ma APC ce ke mulkin jihar ta Kaduna bayan ɗantakararta Uba Sani ya lashe zaɓen gwamna na watan Maris ɗin 2023.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...
X whatsapp