Jam’iyyar APC ta sake tsunduma cikin ruɗani da rabuwar kawuna, inda shugabancin jam’iyyar ya bi sahun wasu gwamnonin da ke fito-na-fito da manufar daina karɓar tsoffin kuɗi Na Shugaba Muhammadu Buhari.
Bayan wani taro da Kwamitin Gudanarwar APC na kasa ya gudanar da yammacin jiya Lahadi, jam’iyyar mai mulki ta yi kira ga shugaban ƙasar ya mutunta umarnin Kotun Ƙoli a kan wannan batu.
Taron wanda mahalartansa suka shafe kimanin tsawon sa’a biyar suna tattaunawa a shelkwatar APC ta ƙasa, ya kammala ba tare da wani dogon bayani kan yadda al’amura suka kaya ba.
Sai dai fuskokin gwamnonin APC da suka halarci taron, babu annuri.
Haka zalika, sanarwar bayan taro da shugaban APC na ƙasa ya karanta bayan fitowarsu, taƙaitacciya ce.
Wannan kuwa na zuwa ne adaidai lokacin da yake kwanaki kalilan a gudanar da babban zaɓe. Sannan al’umma na kokawa da yanayi matsin rayuwa da batun sauya kudi ya jefa su.