Babban jam’iyyar adawa ta PDP, ta bayyana zaben sabon shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Adamu da aka yi a matsayin abin dariya, inda ta ce, jam’iyyar ta tafka babban kuskure.
PDP ta ce zaben da aka yi na cike da badakala kala-kala, kama daga batun yaudara da cin hanci da dai makamtansu.
Babbar Jam’iyyar adawar ta ce za a fuskanci almubazzaranci da jefa jam’iyyar cikin halin kaka ni kayi saboda bisa dukkan alamu jagorancin jam’iyyar ta APC, ya koma hannu wadanda basu san hakkin jama’a ba.
Sannan kuma a cikin shekara guda da ya rage wa shugaba Buhari ya sauka daga mulki, dole Najeriya ta fuskanci wasu sauye sauye marassa ma’ana saboda yanayin yadda shugabancin jam’iyya mai mulkin zai kasance in ji PDP.
Daga nan PDP, ta bukaci ‘ya’yan jam’iyyar APC, da sy fito su wanke sabon shugaban jam’iyyar ta su sanata Adamu, daga zarge zargen cin hancin da ake masa.
PDP ta ce, ya na da kyau, Sanata Adamu ya fito fili ya bayyana wa ‘yan Najeriya dalilinsa na kin bayyana a gaban kotu a lokacin da ake shari’arsa a babbar kotun tarayya.