Jam’iyyar APC reshen jihar Osun, ta maka Gwamna Ademola Adeleke kara kan nada kansa a matsayin kwamishinan ayyuka.
Jam’iyyar da ta shigar da kara a babbar kotun jihar da ke Osogbo, ta kuma kai karar mataimakin gwamnan, Kola Adewusi, kan nadin sa na kwamishinan wasanni da masu bukata ta musamman.
A ranar 19 ga watan Yuli ne Gwamna Adeleke ya bayyana nadin nasa da na mataimakinsa.
Da take adawa da nadin ta bakin lauyanta Sherif Oluyombo, babbar jam’iyyar adawa ta bukaci kotun da ta tantance ko gwamna mai ci zai iya rike wani mukami.
Mai shigar da karar ya koma kan sashe na 192 (2) da na (5) na kundin tsarin mulkin Najeriya, ya roki kotun da ta tantance ko “za a iya nada mutum kwamishina a gwamnatin jiha idan har ba a mika sunan sa ga hukumar ba kuma ta karbe shi. Majalisar domin tabbatar da hakan.”
Wannan dai ba shi ne karon farko da zababbun jami’ai ke rike da mukamai biyu ba.
Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a shekarar 2015 ya nada kanshi ministan man fetur da Ibe Kachikwu a matsayin karamin ministan man fetur sannan kuma Timipre Sylva a wa’adinsa na biyu ba tare da nuna adawa daga jam’iyyarsa ba.
Sakamakon al’amarin na iya hana shugaba Tinubu yin aiki a matsayin minista idan har kotu ta haramtawa zababbun mukamai biyu.