Jam`iyyar APC mai mulkin Najeriya ta faɗa wani sabon ruɗani, bayan gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello, ya yi iƙirarin karɓar jagorancin jam`iyyar a matsayin muƙaddashin shugaba na riƙo.
Wasu rahotanni sun ce, Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da sauke shugaban riƙon jam`iyyar, wato Gwamnan Jihar Yobe, Alhaji Mai mala Buni daga shugabancin jam’iyyar.
Sai dai, wasu ƴan kwamitin riƙon jam’iyyar sun musanta hakan. Masana siyasa dai na cewa, irin wannan dambarwar shugabanci da APC ke ciki na iya rage ƙarfinta a Najeriya.
Duk da cewa an ɗauki lokaci mai tsawo a na ta ce-ce-ku-ce kan jagorancin Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni ke yi wa kwamitin riƙon Jam’iyyar APC na ƙasa.
Wani abu da ya ɗaure kai, shi ne yadda aka wayi gari a ranar Litinin aka ga Gwamnan Jihar Neja Abubakar Sani Bello ya bayyana a matsayin muƙaddashin shugaban jam’iyyar.