Jam’iyya mai mulki ta APC ta aike wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa sanarwar za ta yi zaben shugabannin jam’iyyar na kasa a hukumance.
APC ta aika wasikar a ranar 2 ga Fabrairu kuma INEC ta same ta a ranar 3 ga watan Fabrairu.
Shugaban Kwamitin rikon kwarya na jam’iyya mai mulki, Mai mala Buni, ya sanar da hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, kan hukuncinsu na yin gangamin zaben shugabannin jam’iyyar a ranar da suka tsayar.
Taron gangamin zaben shugabannin jam’iyya mai mulkin za a yi shi ne a ranar 26 ga watan Fabrairu, kuma jam’iyyar ta na da damar kai sanarwar ta ga INEC ne har zuwa ranar 5 ga watan Fabrairu.