fidelitybank

APC ta samu ƙaruwa a zauran majalisar dokokin Kano

Date:

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni a majalisar dokokin jihar Kano, Salisu Ahmad Gwangwazo, ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC a ranar Juma’a.

Dan majalisar ya bayyana matakin nasa ne a wata wasika da ya aikewa shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Alhaji Hamisu Chidari a Kano. majalisar, Malam Uba Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Ahmad-Gwangwazo ya sanya rabe-rabe a shugabancin jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa a dalilin sauya shekarsa.

Sakataren yaɗa labaran majalisar, Malam Uba Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Ahmad Gwangwazo ya sanya rabe-rabe a shugabancin jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa a dalilin sauya shekarsa.

Ya bayyana cewa a cikin wasikar da dan majalisar ya aike wa kakakin mai taken: “Sanarwar sauya shekata daga PDP zuwa APC’, ya mika cewa bangaran ya sanya ba zai yiwu a ci gaba da gudanar da ayyukan jam’iyyar ba.

Abdullahi ya kara da cewa Chidari ya taya Ahmad-Gwangwazo murnar shiga jam’iyyar APC tare da tabbatar masa da cewa jam’iyyar za ta ci gaba da tafiyar da shi da magoya bayansa a kowane hali.

Shugaban majalisar ya kuma tabbatar da cewa, jam’iyyar na gudanar da tsarin da ya kunshi kowa da kowa, ya kara da cewa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar suna da ruwa da tsaki a ci gaban jihar.

Abdullahi ya kuma ruwaito shugaban majalisar na cewa akwai alamun jam’iyyar APC mai mulki za ta ci gaba da rike madafun iko a jihar a zaben 2023 mai zuwa.

Bayan sauya shekar Ahmad-Gwangwazo, majalisar tana da ‘yan majalisar APC 20 da kuma 11 na PDP.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp