Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birni a majalisar dokokin jihar Kano, Salisu Ahmad Gwangwazo, ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC a ranar Juma’a.
Dan majalisar ya bayyana matakin nasa ne a wata wasika da ya aikewa shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Alhaji Hamisu Chidari a Kano. majalisar, Malam Uba Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Ahmad-Gwangwazo ya sanya rabe-rabe a shugabancin jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa a dalilin sauya shekarsa.
Sakataren yaɗa labaran majalisar, Malam Uba Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Ahmad Gwangwazo ya sanya rabe-rabe a shugabancin jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa a dalilin sauya shekarsa.
Ya bayyana cewa a cikin wasikar da dan majalisar ya aike wa kakakin mai taken: “Sanarwar sauya shekata daga PDP zuwa APC’, ya mika cewa bangaran ya sanya ba zai yiwu a ci gaba da gudanar da ayyukan jam’iyyar ba.
Abdullahi ya kara da cewa Chidari ya taya Ahmad-Gwangwazo murnar shiga jam’iyyar APC tare da tabbatar masa da cewa jam’iyyar za ta ci gaba da tafiyar da shi da magoya bayansa a kowane hali.
Shugaban majalisar ya kuma tabbatar da cewa, jam’iyyar na gudanar da tsarin da ya kunshi kowa da kowa, ya kara da cewa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar suna da ruwa da tsaki a ci gaban jihar.
Abdullahi ya kuma ruwaito shugaban majalisar na cewa akwai alamun jam’iyyar APC mai mulki za ta ci gaba da rike madafun iko a jihar a zaben 2023 mai zuwa.
Bayan sauya shekar Ahmad-Gwangwazo, majalisar tana da ‘yan majalisar APC 20 da kuma 11 na PDP.