Kwamitin tantancewar jamâiyyar All Progressives Congress (APC) ya wanke babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami daga tsayawa takarar gwamnan jihar Kebbi a zaben 2023.
Wata takarda da ke nuni da izinin Malami na tsayawa takara, ta janyo cece-kuce a fagen siyasa tun bayan da AGF ta janye aniyarsa ta tsayawa takarar gwamna, domin ya ci gaba da rike mukamin minista.
A makon da ya gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin cewa duk masu rike da mukaman siyasa da su yi murabus kafin su tsaya takara a zabe mai zuwa.
Babu tabbas ko Mista Malami ya mika takardar murabus dinsa ne domin ya ci gaba da neman sa ta siyasa bisa bin umarnin Buhari ko kuma yana jiran fassarar kotun koli ta sashe na 84 (12) na dokar zabe ta 2022.
Malami bai samu jin ta bakinsa ba saboda har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a samu layinsa da na mai magana da yawunsa Umar Gwandu ba.
Wasu masu rike da mukaman siyasa sun tayar da hankulan jama’a bayan sun sabawa ka’idojin siyasa don neman mukaman zabe ba tare da sun yi murabus ba.