Hukumar zaben jihar Ebonyi, ta bayyana ‘yan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin wadanda suka lashe dukkanin kujerun shugabanni da kansiloli a zaben kananan hukumomin da aka gudanar a ranar Asabar.
Hukumar ta ce, jam’iyya mai mulki ta lashe zaben a dukkan kananan hukumomi 13 na jihar.
Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar (EBSIEC), Mista Jossy Eze, ne ya bayyana hakan a Abakaliki ranar Lahadi a hedikwatar hukumar.
A cewar Eze, APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 13 da na kansiloli 171.
Ya yabawa al’ummar kasar da suka tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana.
“A bisa ikon da doka ta ba ni, na bayyana sakamakon shugabancin kowace karamar hukuma 13 kamar haka.
Sauran zababbun shugabannin APC sun hada da Chinedu Uburu, karamar hukumar Ebonyi; Chidiebere Uzor, Onicha LGA; Chinonso Ajah, Ohaozara LGA; Ibiam Nnajiofor, Afikpo North da Ekuma-Nkama Chima, Afikpo South.