fidelitybank

APC ta kafa kwamitin sulhu na rikicin da ya dabaibaye jihar Oyo

Date:

A wani yunkuri na sasanta rikicin da suka taso daga majalissar dokokin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da na ‘yan takara a jihar Oyo gabanin zaben 2023, jam’iyyar ta kafa kwamitin sulhu na mutum 24.

Shugaban jam’iyyar a jihar Isaac Omodewu ne ya kaddamar da kwamitin a ranar Asabar a sakatariyar jam’iyyar dake Oke-Ado, Ibadan, babban birnin jihar.

Shugaban kwamitin sulhun shi ne Cif Olufemi Lanlehin yayin da Sakataren shi ne Alhaji Tajudeen Olanite.

Sauran mambobin kwamitin sun hada da Hadji Dr Ameed A Ayinde, Hon Lasun Adebunmi, Alhaji Gbadamosi Abu Adejare, Cif Timothy Alarape Jolaoso, Injiniya Oladayo Lawal, Cif Badmos Bukola, Sunday Ajadi, Hon Chief S. O. Olaoye, Balogun Gaphar Oyetola da Erelu Funke Olayanju.

Pastor Adewale Adepoju, Alhaji Kakako Ayinla, Alhaji Ramon Aderemi Sadiq, Hon Olorode Samuel Oluade, Otunba Kunle Folarin, Akande Abass, Alhaji Kareem Adebayo, Dr Adepeju Esan, Tunde Ajibola, Remi Olalekan, Injiniya Oke Kolawole da Hafeez Omobolaji Repete.

Da yake kaddamar da kwamitin, Shugaban jam’iyyar APC na Oyo ya bukaci ‘ya’yan jam’iyyar da su bai wa kwamitin hadin kai don ganin an shawo kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp