fidelitybank

APC ta jefa ‘yan Najeriya cikin wahala – Atiku

Date:

Tsohon mataimkain shugaban kasa, Atiku Abubakar ya gargaɗi al’ummar jihar Edo da su guji zaɓar ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe ranar Asabar 21 ga watan Satumban, 2024.

Atiku ya bayyana haka ne a shafinsa na X ranar Laraba, inda ya shawarci mazauna jihar da su zaɓi ɗan takara da ya cancanta wanda zai kai jihar gaba.

Ya ce APC ta jefa al’umma cikin mawuyacin hali kuma ba ta jin koke-kokensu.

“A matsayinku na ƴan jihar Edo, ku yi amfani da ƴancinku na yin zaɓe don watsi da rashin shugabanci mai kyau da kuma kawo sauyi. Ku tabbata kun zaɓi cancanta.

“APC ta saba yi wa mutane daɗin baki lokacin yaƙin neman zaɓe, amma da zarar sun yi nasara sai su sauya manufa – jam’iyyar cike take da masu son mulki kawai ba tare da sanya buƙatun al’umma a gaba ba,” in ji Atiku.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriyar ya ce jam’iyyar ta sauka daga tsarin shugabanci nagari tare da yin watsi da buƙatun talakawa.

Ya ce sun jefa ƴan Najeriya cikin wahala da kunshi karkashin jagorancinsu.

Don haka ya buƙaci ƴan jihar ta Edo da su fito su zaɓi ɗan takarar jam’iyyar PDP Dr. Asue Ighodalo wanda a cewarsa shi zai kai jihar gaba.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp