Rahotanni masu karfi sun tabbatar da cewa, jam’iyyar APC ta fara zawarcin tsagin Sanata Rabiu Kwankwaso na PDP.
Tsohon gwamnan Kano, Sanata Kwankwaso, na É—aya daga cikin manyan ‘yan siyasa masu dumbin magoya baya, musamman a Arewa.
Rahoto ya nuna cewa, akwai alamun takun siyasa dake nuna cewa, tsohon Sanatan Kano ta tsakiya ka iya komawa APC.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, bangaren mataimakin shugaban Ć™asa, Farfesa Yemi Osinbajo, sun tuntubi Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, domin haÉ—a kai a takarar 2023. Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon ministan tsaro a Najeriya, a halin yanzun babban jigo ne a jam’iyyar PDP.