Jam’iyyar APC ta yi nasarar doke jam’iyyar PDP, bayan samun nasara a dukkanin kananan hukumomi 31, inda aka bayyana sakamakon zaben, in ji Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KTSIEC).
Sakataren hukumar, Alhaji Lawal Faskari, wanda ya bayyana hakan da sanyin safiyar Talata a Katsina, ya ce, ba a kammala zaben a kananan hukumomin Daura da Funtua ba.
Ya kuma ce, an soke zaben a karamar hukumar Dutsin-Ma, saboda wasu kalubale, inda ya ce, an gudanar da zaben cikin lumana a duk sauran yankunan.