Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta dakatar da yakin neman zaben gwamnan jihar Kogi a ranar 11 ga watan Nuwamba.
An dakatar da yakin neman zaben ne domin nuna girmamawa ga Ms Khadijat Yahaya, ‘yar jam’iyyar da ta mutu bayan harin da wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka kai musu.
Mista Kingsley Fanwo, mai magana da yawun hukumar yakin neman zaben jihar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata.
Ana zargin Khadijat ta rasa ranta ne bayan wani rikici da ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da na APC a Kotonkarfe a ranar 29 ga watan Satumba.
A halin da ake ciki, dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar APC, Alhaji Usman Ododo, ya ziyarci iyalan marigayiyar a Kotonkarfe a ranar Talata domin jajanta musu bisa rasuwar ta.
Ododo ta bayyana kaduwarsa da rasuwar ta, sannan ta yi addu’ar Allah ya jikan ta.