fidelitybank

APC ta dage gangamin yakin neman zaben ta na Laraba

Date:

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC a ranar Talata, ta ce, ta dage fara yakin neman zaben ta da aka shirya yi a ranar Laraba.

Darakta-Janar na kungiyar yakin neman zaben Tinubu/Shettima kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong ne ya bayyana hakan.

Sanarwar ta bayyana cewa, daidaita jadawalin ya biyo bayan matakin fadada jerin sunayen majalisar yakin neman zaben domin samun karin masu ruwa da tsaki.

Gwamnan ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon ranar da za a fara gasar.

Sanarwar ta ce; “Ku tuna cewa tun da farko mun shirya tattaki da addu’o’in zaman lafiya a ranar Laraba, 28 ga Satumba, 2022, don fara yakin neman zaben shugaban kasa na 2023 a hukumance.

“Mun kuma sanar da cewa mambobin kwamitin yakin neman zaben sun kai rahoto a hedikwatar yakin neman zaben a ranar domin karbar wasikun nadi.

“Duk da haka, saboda fadada jerin sunayen don samun karin masu ruwa da tsaki da bukatun cikin gidan APC, mun yanke shawarar daidaita jadawalin wadannan ayyuka domin tabbatar da cewa kowa yana cikin jirgin kafin a fara ayyukan a hukumance.

“Saboda haka, ayyukan da aka sanar a baya na ranar 28 ga Satumba ba za su ci gaba ba.”

Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa watakila hakan baya rasa nasaba da zanga-zangar da gwamnonin jam’iyyar APC suka yi a kan jerin yakin neman zaben.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp