fidelitybank

APC ta caccaki PDP akan dakatar da tsohon gwamnan Enugu mai goyon bayan Tinubu

Date:

Jam’iyyar All Progressives Congress, APC ta caccaki jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP kan dakatar da dan majalisar dattawa mai wakiltar Enugu ta Gabas, Sanata Chimaroke Nnamani.

DAILY POST ta tuna cewa a ranar Juma’a ne kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na kasa, NWC ya dakatar da tsohon gwamnan Enugu bisa zargin ya goyi bayan Tinubu.

Dakatarwar ba za ta rasa nasaba da matakin da dan majalisar ya dauka na goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu a zabe mai zuwa ba.

Chimaroke ya sha bayyana a lokuta da dama, cewa zai yi wa tsohon gwamnan Legas aiki ne a sakamakon cutar da dan takarar jam’iyyar sa, Atiku Abubakar.

Da yake mayar da martani, mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo ya ce,

 

dakatarwar ba za ta yi wani tasiri ga Chimaroke ba.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na twitter, karamin ministan kwadago, samar da ayyuka da samar da ayyukan yi ya yi wa jam’iyyar adawa, yana mai cewa PDP na rugujewa a tsakiyar yakin neman zabe.

Tweet din ya ce, “Bata lokaci; yanke hanci don tozarta fuskarki. Dakatarwar ba ta da wani tasiri a wannan lokaci, domin doka ta ce ya ci gaba da zama dan takarar jam’iyyar.

“Jam’iyyar da ke rugujewa a tsakiyar yakin neman zabe! Rashin mutunta kundin tsarin mulkinsa ne yanzu yake farautarsa”!

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp