Jam’iyyar APC mai mulki ta bayyana ranar karshe da ministoci da masu rike da mukaman gwamnati za su ajiye ayyukansu a matakan tarayya da na jihohi idan suna son tsayawa takara a zabukan da ke tafe.
Jami’an gwamnatin za su ajiye aiki zuwa ranar Asabar 30 ga watan Afrilu.
Matakin ya shafi wasu ministocin gwanatin Buhari kamar ministan sufuri Chibuike Rotimi Amaechi da kwadago Chris Nigige, suna ciki jami’an da suka bayana aniyarsu ta tsayawa takara.
Sashe na 3(i) na dokar jam’iyyar APC kan tsayar da ‘yan takara a zaben 2023 na cewa: “Ba a yarda wani jami’in da ke rke da mukami a kowane matakin gwamnati ya zama deleget ko a zabe shi domin fitar da ‘yan takara.”
Jadawalin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta fitar ya tsara cewa jam’iyyun siyasa na da zuwa ranar 3 ga watan Yuni domin su mika ma hukumar mutanen da suka tsayar a zabukan da ke tafe.”