fidelitybank

APC ta amince ta shigar da Kannywood cikin yakin zaben ta

Date:

Gabanin zaben shugaban kasa na 2023, Darakta-Janar na Jam’iyyar APC Campaign Council, Gwamna Simon Lalong, ya amince da shigar da wasu ‘yan Kannywood cikin majalisar.

Lalong ya bayyana hakan ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Dr Makut Maham, a Jos babban birnin jihar.

Shugaban yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC ya ce hada ’yan fim din na da nufin zurfafa shigar da masu fasahar kere-kere daga yankin Arewa a yakin neman zabe.

Ya ce kungiyar ta Kannywood ta na da Abdul-Mahmud Amart a matsayin Darakta, Ismail Afakallah a matsayin mataimakin darakta da Sani Mu’azu a matsayin Sakatare, tare da sauran shugabannin da ke jagorantar bangarori daban-daban.

Lalong ya ce amincewar ta biyo bayan ziyarar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya kai Kano, inda ya gana da ‘ya’yan kungiyar.

Ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya yi alkawarin cewa za a bai wa ‘yan Kannywood damar shiga cikin yakin neman zabe domin baje kolin basirarsu tare da taimakawa jam’iyyar ta lashe zabe mai zuwa, kamar yadda NAN ta ruwaito.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp