Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) shiyyar Arewa maso Yamma, sun kuduri aniyar amincewa da zaben tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima, a matsayin mataimaki ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
An dauki wannan kudiri ne a Dutse, babban birnin jihar Jigawa, lokacin da mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa (Arewa maso Yamma), Salihu Moh Lukman, ya jagoranci masu ruwa da tsaki a rangadin yankin.
Sanarwar da Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Yamma, Malam Musa Mailafiya Mada, ya fitar a Abuja bayan kammala rangadin, ya bayyana cewa sun kuma tattauna dabarun kawo nasara a jam’iyyar.
“Batun daga cikin batutuwan da aka tabo a taron shi ne fitowar Kashim Shettima a matsayin abokin takarar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Asiwaju Tinubu da kuma yadda ya kamata shiyyar ta tsayar da kanta wajen kawo wa jam’iyyar nasara a dukkan matakai.
Mahalarta taron sun kuduri aniyar yin aiki da hadin kan ‘ya’yan jam’iyyar tare da kara himma wajen zaburar da ‘yan Najeriya su zabi Bola Tinubu da Kashim Shettima a matsayin shugaban kasa da mataimakin shugaban kasar Najeriya da kuma dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC a zaben 2023. karanta.