fidelitybank

APC na zawarcin Kwankwaso da mabiyansa – Ganduje

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki ta shiga zawarcin kananan jam’iyyun adawa ciki harda NNPP ta Rabi’u Musa Kwanwkaso da mabiyansa.

Shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya shaida wa BBC cewa tuni suka aike da goron gayyata ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Rabiu Musa Kwankwaso.

Ganduje ya yi waÉ—annan kalamai ne a wani taro da ya jagoranta da shugabannin jam’iyyarsa ta APC a jihar Kano, inda ya ce dama can uwa É—aya uba É—aya suke da su Kwankwason.

A cewa Ganduje, “Wannan ya zama dole saboda a matsayina na shugaban jam’iyyar APC na kasa ina zagayawa jihohi, sanatoci sun shigo cikin wannan jam’iyya tamu ‘yan majalisar tarayya sun shigo wannan jam’iyya tamu, haka nan kuma gwamnoni.

Shugaban APC ya ce nan gaba ma akwai wadanda za su shigo cikin jam’iyyar, kuma wannan dalili ne ya sa ya fito yana neman hadin kai daga jiharsa ta Kano.

“Na ma kira wasu na waje ballantana namu na gida” in ji shi.

Sai dai shugaban jam’iyyar APC ya ce kawo yanzu ba su rubutawa jagoran jam’’iyyar NNPP da gwamnan jihar Kano wasika a hukumance ba game da wannan kiran da suka yi mu su.

A cewarsa suna son É“angaren Kwankwaso ya nuna sha’awar shiga jam’iyyarsu ta APC kafin a je matakin aike wasika.

Wannan bukata ta APC na zuwa ne adaidai lokacin da jama’a da dama ke nuna shaku kan ba lallai tafiyar tayi kyau ba tsakanin Kwankwaso da Ganduje a inuwa guda.

Amma Ganduje ya nuna kwarin gwiwa tare da tunasar da cewa, “ai dama can gidanmu É—aya, dama can Ubanmu É—aya, an samu rarrabuwar kai, yanzu kuma idan Allah ya sake haÉ—awa, to me ya fi wannan daÉ—i”.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp