Yayin da ke ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen gwamnan jihar Edo da aka gudanar ranar Asabar 21 ga watan Satumba, manyan jam’iyyun siyasar jihar biyu na ci gaba da yin kankankan.
Shugaban Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Minna, Farfesa Farouk Adamu Kuta ne babban jami’i tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar.
Babbar Jami’ar INEC ta ƙasa da ke kula da zaɓen, Farefesa Rhoda Gumus ta ce a halin yanzu akwai sakamakon ƙananan hukumomi 14 zuwa 15 a zauren tattara sakamakon.
Kawo yanzu an bayyana sakamakon ƙananan hukumomi 16, yayin da sakamakon ya nuna cewa jam’iyyar PDP mai mulkin jihar ta samu ƙananan hukumomi biyar, inda ta lashe ƙananan hukumomi huɗu daga ciki, inda APC lashe ƙananan hukumomi 11 daga ciki.
Ga sakamakon kamar haka:
Ƙaramar hukumar Igueben
APC- 5907
PDP – 8470
Ƙaramar hukumar Esan ta Yamma
APC – 12952
PDP – 11004
Ƙaramar hukumar Owan ta Yamma
APC – 12277
PDP – 11284
Ƙaramar hukumar Uhunmwonde
APC – 8776
PDP – 9339
Ƙaramar hukumar Ovia ta Arewa maso
APC – 13225
PDP – 15311
Ƙaramar hukumar Esan ta Kudu maso
APC – 8398
PDP – 14199
Ƙaramar hukumar Egor
APC – 16760
PDP – 14658
Ƙaramar hukumar Akoko-Edo
APC – 34847
PDP – 15865
Ƙaramar hukumar Esan ta Tsakiya
APC – 10990
PDP – 8618
Ƙaramar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas
APC – 10648
PDP – 12522
Ƙaramar hukumar Ovia ta Kudu maso Yamma
APC – 10150
PDP – 10260
Daga BBC.