fidelitybank

APC da Ganduje ba za su samu galaba a Ondo ba – Makinde

Date:

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da shugabanta na kasa, Abdullahi Ganduje, za su kadu da sakamakon zaben gwamnan jihar Ondo da aka gudanar a ranar 16 ga watan Nuwamba.

Makinde ya kuma ce jam’iyya mai mulki za ta fuskanci shan kaye a zabukan da za a yi a shiyyar Kudu maso Yamma.

Yayin da yake jaddada cewa jam’iyyar PDP za ta kayar da jam’iyya mai mulki, Makinde, wanda shi ne shugaban jam’iyyar PDP a yankin Kudu maso Yamma, ya jaddada cewa APC ta zama makiyan ‘yan Nijeriya.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, ya bayyana a kwanakin baya a Akure, babban birnin jihar Ondo, cewa nan ba da dadewa ba APC za ta kwace jihohin Kudu maso Yamma bayan lashe zaben Ondo.

Hakazalika, Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya yi ikirarin a ranar Laraba cewa PDP ta mutu a jihar.

Gwamnan jihar Oyo wanda ya jagoranci gangamin yakin neman zaben jam’iyyar PDP zuwa yankin Akoko na jihar Ondo, ya bayyana cewa har yanzu PDP na nan daram a jihar Ondo.

A cewarsa, PDP ta kuduri aniyar samun nasara a zaben gwamna. Ya jaddada cewa Ganduje da Aiyedatiwa za su yi mamakin sakamakon zaben gwamna mai zuwa.

“Idan so ne dawakai, da kowa zai hau su. Zan iya gaya muku cewa mutanen Kudu maso Yammacin Najeriya sun fi wayo musamman a Jihar Ondo, inda muke nan (Akoko area).

“Kuna iya ganin taron; dubi sha’awa. A ranar 16 ga Nuwamba, za su gaya masa (Ganduje) cewa Jihar Ondo da kuma Kudu maso Yamma na PDP ne. To, magana, sun ce arha ne. Kuna iya faɗi duk abin da kuke so da bakin ku.

“Mutanen Jihar Ondo za su yi magana da babbar murya a ranar 16 ga Nuwamba, 2024, sannan dukkan mu a kasar nan za mu ji shi da babbar murya.”

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp