Bayan da hukumar zaɓe ta (INEC) ta sanar da sakamakon ƙananan hukumomi 18 a zaɓen gwamnan jihar Kogi, ɗan takarar jam’iyyar APC, Usman Ahmed Ododo ne ke kan gaba.
Yanzu ana jiran sakamako daga ƙananan hukumomi uku.
Ƙananan hukumomin da ake jiran sakamakonsu a zaɓen na gwamnan su ne:
- Lokoja
- Igalamela- Odolu
- Ibaji
Kogi na da ƙananan hukumomi 21 a jimilla.
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ce ke da hurumin sanar da wanda ya yi nasara bayan kammala tattara sakamakon zaɓen.