Gwamatin jihar Kano ta ce ba za ta lamince da hukuncin da kotun a Abuja ta yi na rushe zaben shugabancin jam’iyyar APC da tsagin gwamnati ya gudanar.
Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Barista Musa Abdullahi Lawal ne ya shaida hakan ga manema labarai ranar Talata.
Ya ce”Lauyoyin gwamnati sun fara nazaratar hukuncin tare da daukar matakin da ya da ce a kai, mun yi mamakin hukuncin, kuma ba za mu karbe shi ba, lokacin da a ka gudanar da zabukan a matakan mazabu babu wadanda a ka yi su daban. Domin haka ba mu ga dalilin da ya sa aka rushe shugabanci Abdullahi Abbas”.
Ya kuma ce, za su duba yadda aka shigar da karar har aka samu, sakamakon zabukan da aka gudanar har suka gabatarwa kotu da ta amince dasu.