fidelitybank

APC ba ta tsoron hadakar abokan hamayya – Orji Uzor Kalu

Date:

Sanata mai wakiltan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ba ta tsoron jam’iyyar adawa.

Kalu ya ce gamayyar jam’iyyun adawa na da ‘yancin kalubalantar jam’iyyar APC, amma jam’iyya mai mulki za ta ci gaba da mai da hankali wajen gudanar da ayyukan ta.

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ne ke jagorantar kafa kungiyar hadin gwiwa.

Gamayyar a cewar El-Rufai za ta tabbatar da cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya fadi zaben shugaban kasa a 2027.

Sai dai tsohon gwamnan na jihar Abia ya ce nan ba da dadewa ba ‘yan Najeriya za su fara yaba ayyukan gwamnatin APC da ta mayar da hankali kan harkokin mulki.

Kalu ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Talata.

Ya ce: “Ba mu yi barci ba, APC ba ta da dalilin tsoro, mu ne jam’iyya mai mulki kuma mai kishin ci gaban Nijeriya.

“Da yawa daga cikinmu muna saka hannun jari a masana’antu don samar da ayyukan yi fiye da siyasa.

“Wadannan amincewa ba wai tsoro ba ne, sakamakon jajircewar shugaban kasa ne ya yanke shawara da kawo sauyi.

“’Yan adawa suna da ‘yancin kalubalantarmu, aikinsu kenan, amma mu namu shine samar da sakamako, kuma muna yin haka.

“A cikin lokaci mai tsawo, ‘yan Najeriya za su fahimci zabukan da wannan gwamnatin ta yi.”

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp