Sanata mai wakiltan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ba ta tsoron jam’iyyar adawa.
Kalu ya ce gamayyar jam’iyyun adawa na da ‘yancin kalubalantar jam’iyyar APC, amma jam’iyya mai mulki za ta ci gaba da mai da hankali wajen gudanar da ayyukan ta.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ne ke jagorantar kafa kungiyar hadin gwiwa.
Gamayyar a cewar El-Rufai za ta tabbatar da cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya fadi zaben shugaban kasa a 2027.
Sai dai tsohon gwamnan na jihar Abia ya ce nan ba da dadewa ba ‘yan Najeriya za su fara yaba ayyukan gwamnatin APC da ta mayar da hankali kan harkokin mulki.
Kalu ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Talata.
Ya ce: “Ba mu yi barci ba, APC ba ta da dalilin tsoro, mu ne jam’iyya mai mulki kuma mai kishin ci gaban Nijeriya.
“Da yawa daga cikinmu muna saka hannun jari a masana’antu don samar da ayyukan yi fiye da siyasa.
“Wadannan amincewa ba wai tsoro ba ne, sakamakon jajircewar shugaban kasa ne ya yanke shawara da kawo sauyi.
“’Yan adawa suna da ‘yancin kalubalantarmu, aikinsu kenan, amma mu namu shine samar da sakamako, kuma muna yin haka.
“A cikin lokaci mai tsawo, ‘yan Najeriya za su fahimci zabukan da wannan gwamnatin ta yi.”