fidelitybank

APC ba ta amince da sakamakon zaben gwamnan jihar Bauchi ba

Date:

Jam’iyyar APC a jihar Bauchi, ta yi watsi da sakamakon zaɓen gwamnan jihar wanda ya bai wa Bala Mohammed na jam’iyyar PDP wanda hukumar zaɓen ƙasar ta sanar cewa ya lashe a karo na biyu.

A taron manema labarai da ta kira ranar Litinin, ɗan takarar jam’iyyar Air Marshal Sadiq Baba Abubakar mai ritaya ya ce an tafka kura-kurai a zaɓen da dama waɗanda suka tilasta wakilan jam’iyyar ƙin sanya hannu kan takardar shaidar sakamakon zaɓen.

Jam’iyyar APC a jihar ta yi zargin cewa an tabka maguɗi bayan kura-kurai da ta yi zargi an samu, don haka ta buƙaci hukumar zaɓen ƙasar ta soke sakamakon zaɓen da aka gudanar a ƙananan hukumomin Alƙaleri da Kirfi da Toro da Warji da Zaki.

Sannan ta bukaci bayan soke zaɓen, a kuma bayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba.

Air Marshall Abubukar Baba Sadique mai riyata ya yi zargin cewa an razana mutane da makamai, sannan ya yi zargin cewa jam’iyyar PDP ta sayi ƙuri’u a rumfunan zaɓen.

Ya ce wakilan jam’iyyarsu sun ƙi saka hannu a kan sakamakon da suka yi zargin an tafka maguɗi, amma duk da haka an sanar da sakamakon zaɓen.

Sannan ya ce za su yi nazari da kuma tattaunawa da al’ummarsu kan sakamakon zaɓen kafin ɗaukar mataki na gaba.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp