Jigon jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Alhaji Umaru Adamu, ya bayyana fargabar cewa jam’iyyar za ta iya fuskantar babban kalubale idan har sai an sake zaben gwamna.
Adamu ya koka da yadda aka mayar da hankali sosai a bangaren cikin gida a jam’iyyar, inda ya ce ta sha kaye sosai a zaben 2023 sakamakon rikicin cikin gida daya.
“Babu shakka akwai munanan rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar a jihar saboda daukakar siyasar shugabannin jam’iyyar,” inji shi.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a Gusau, babban birnin jihar, inda ya jaddada cewa a hankali jam’iyyar APC na kara samun karbuwa a jihar.
A cewarsa, jam’iyyar na bukatar gyara sosai domin samun damar ci gaba, yana mai nuni da cewa babu wata jam’iyyar siyasa da za ta yi ikirarin cewa tana da girma ba tare da hadin kan manyan ‘ya’yanta ba.
Ya kara da cewa “Idan har za a sake zaben gwamna a jihar, APC za ta shiga cikin babbar matsala sakamakon rikicin cikin gida a cikin jam’iyyar.”
Adamu ya shawarci dattawan jam’iyyar da su sake haduwa tare da kulla kawancen siyasa da sauran jam’iyyu domin samun damar fafatawa da jam’iyyar PDP mai mulki a jihar, inda ya ce idan ba haka ba jam’iyya mai mulki za ta mayar da APC koma baya. .