fidelitybank

APC a shirye take ta karbi Kwankwaso har idan ya bar NNPP – Ganduje

Date:

Sabon zababben shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, ya ce jam’iyya mai mulki a shirye take ta karbi bakuncin shugaban jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na kasa, Rabiu Kwankwaso, idan har yana so ya sauya sheka.

Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano, ya bayyana matsayar sa a yayin tattaunawa da wasu zababbun kungiyoyin yada labarai a Kano a daren ranar Asabar.

Shugaban jam’iyyar APC ya bayyana cewa a yanzu shi ne ke tafiyar da al’amuran jam’iyyar, inda ya jaddada cewa matsayinsa ya sa Kwankwaso ya samu saukin komawa jam’iyyar mai mulki idan ya so.

Ya bayyana Kwankwaso a matsayin dan siyasa nagari wanda ya rike mukamai da dama a jihar da kasa baki daya.

Ya ce: “Ba wanda zai ce Kwankwaso ba dan siyasa ba ne; aƙalla ya kasance gwamnan Kano na wa’adi biyu, duk da cewa a cikin wa’adin mulkinsa ya lalace; ya kasance Ministan Tsaro, duk da cewa bai san menene tsaro ba; kuma ya taba zama Sanata, duk da cewa bai taba cewa komai ba tsawon zamansa a wurin.

“Amma idan har yana son sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, kofar mu a bude take, musamman a yanzu da wani dan jiharsa ya zama shugaban jam’iyyar; zai yi masa sauki ya shiga harabar,” ya kara da cewa.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp