Janne Andersson ya bayyana cewa, ya tattauna da hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF) kan aikin kocin Super Eagles.
Hukumar NFF na ci gaba da farautar sabon kocin Super Eagles sama da watanni biyu bayan tsohon dan wasan gefe na kasa da kasa, Finidi George ya bar mukamin.
Rahotanni sun bayyana cewa Andersson wanda tsohon kociyan kungiyar kwallon kafa ta kasar Sweden ne ya amince zai horar da zakarun nahiyar Afrika har sau uku.
Gogaggen gwanin ya bayyana sha’awar sa ta kocin Super Eagles.
“Babban al’ummar ƙwallon ƙafa ce. Zan iya tabbatar da cewa na yi tattaunawa da Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya,” kamar yadda ya shaida wa jaridar Sweden, Expressen.
“Babban al’ummar kwallon kafa ce don haka na yi matukar farin ciki da kasancewa mai horar da ‘yan wasanta na gaba.
“Tattaunawar tana gudana kuma ba na son in faɗi fiye da haka. Na daɗe a cikin wannan masana’antar kuma na san cewa abubuwa na iya faruwa ta hanyoyi daban-daban. Don haka za mu ga abin da zai faru nan gaba.”