fidelitybank

Ana ƙoƙarin shafawa Manjo Janar Erema kashin kaji cewa ya sayi gida a Amurka da kuɗin sata – Sojoji

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce, ta lura cike da damuwa da kokarin wasu mutane na birkita tunanin jama’a da gangan, ta hanyar yunkurin shafa kashin kaji da jamhuru ga wani babban hafsanta, Manjo Janar Erema Akerejola, kan zargin sayen gida a Amurka da kudaden almudahanar kwangila.

Ta ce ba shakka, an sayi gidan da ake magana kansa a Amurka, amma bisa yarjejeniyar rancen gina gida da ake biya wata-wata, kuma har yanzu matar Manjo Janar Erema Akerejola wadda mazauniyar Amurka ce, tana ci gaba da biya.

Rundunar sojin Najeriya a sanarwar da daraktan hulda da jama’anta Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce kokarin nuna cewa mai gidan asali ya/ta fito ne daga gidan talakawa, wani kokarin kunyata dukkan ‘yan Najeriya ne masu aiki tukuru, wadanda suka tabuka wani abin kirki a rayuwa.

Sanarwar ta ce muhimmin abu ne a lura cewa an nada Janar Erema Akerejola kan mukamin Babban Hafsan Tsara Dabarun Sufuri da Gyare-gyare na rundunar sojin Najeriya ne wata shida da ya wuce, gidan kuma da ake magana kansa, an mallake shi ne shekara 12 a baya.

Ta kalubalanci mutumin da ya buga labarin a jaridar Sahara Reporters ta intanet da cewa bai iya gabatar da wata shaida ba, in ban da kalmomin wata majiya da bai iya bayyana sunanta ba, wadda ga alama a cewar rundunar sojojin Najeriya na cike da hauci, idan ma akwai ta a zahiri.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp