fidelitybank

Ana zargin Ɗan Sanda ya harbe abokin aikin sa a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sanda a Jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani jami’inta mai suna Koufr Basiru Ibrahim da ake zargin abokin aikinsa Sufeta Hussaini Sani ya harba a lokacin da suke kan hanyar su ta komawa wajen aiki a jihar Katsina.

Rundunar ta ce lamarin ya faru ne a lokacin da bindigar da ke hannun Hussaini ta harba kanta, inda ta samu marigayin a ciki kuma bayan kai shi asibiti ya rasu.

Wasu da lamarin ya faru a kan idonsu sun ce a gefen titin kurnar Asabe da ke birnin Kano aka yi harbin.

Tuni rundunar ta ce ta kama dan sandan da ya yi harbin don gudanar da bincike a kan afkuwar lamarin.

Wannan ne dai karon farko a 2022 da wani dan sanda ya kashe abokin aikinsa a Kano, in da a 2021 ma aka samu wani dan sanda a jihar da ya harbe abokin aikinsa saboda ya yi masa dariya. A cewar BBC.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp