fidelitybank

Ana zaman ɗarɗar a Imo bayan an kashe jami’an tsaro

Date:

Ana zaman dar-dar a yankin Umualumaku da ke karamar hukumar Ehime Mbano a jihar Imo, biyo bayan kashe jami’an tsaro da ba su wuce takwas ba da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka yi.

Wadanda suka mutun sun hada da sojoji, jami’an ‘yan sanda, da jami’an tsaron farin kaya na Najeriya.

Lamarin da ya afku a safiyar ranar Talata, ya haifar da fargaba, inda mazauna yankin suka kara tada jijiyoyin wuya.

Rahotanni sun ce an kai wa wasu motocin jami’an tsaro guda biyu hari tare da kona musu wuta.

Wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaidawa DAILY POST cewa an aike da karin tawaga zuwa wurin da lamarin ya faru a kokarin damke wadanda suka aikata laifin tare da kwato gawarwakin jami’an tsaron da suka mutu.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Henry Okoye, ya tabbatar da faruwar lamarin amma ya nemi a ba shi lokaci domin samun cikakken bayani kan wannan mumunan lamarin.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp