Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Amnesty International a Najeriya, ta zargi hukumomin Najeriya da yunkurin yin rufa-rufa kan kisan gillar da aka yi wa fararen hula sama da 120 a harin da sojoji suka kai a Kaduna.
Kungiyar ta ce bayanai masu cin karo da juna da sojoji suka bayar ya nuna kokarinsu na ganin an ɓoye lamarin ba tare da wani bincike ko yin adalci ga rayukan da aka rasa ba.
Zargin na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan kungiyar Isa Sanusi ya fitar.
An kashe mutanen kauyen da dama tare da raunata wasu da dama sakamakon wani bam da aka harba na rundunar sojojin Najeriya.
Sanusi ya soki sojoji da fitar da bayanai masu karo da juna kan lamarin Tudun Biri.
“Bayani masu cin karo da juna da sojojin Najeriya suka bayar ya zuwa yanzu sun nuna rashin mutunta rayukan fararen hula tare da bayar da shawarar kokarin da hukumomi ke yi na boye wadannan munanan take hakkin dan Adam. Hare-haren jiragen sama da ke haifar da kisa ga fararen hula na zama na yau da kullun. Wannan sam ba za a amince da shi ba,” inji Sanusi