fidelitybank

Ana yunƙurin yin rufa-rufa kan kasar gillar fararen hular Tudun Biri – Amnesty

Date:

Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Amnesty International a Najeriya, ta zargi hukumomin Najeriya da yunkurin yin rufa-rufa kan kisan gillar da aka yi wa fararen hula sama da 120 a harin da sojoji suka kai a Kaduna.

Kungiyar ta ce bayanai masu cin karo da juna da sojoji suka bayar ya nuna kokarinsu na ganin an ɓoye lamarin ba tare da wani bincike ko yin adalci ga rayukan da aka rasa ba.

Zargin na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan kungiyar Isa Sanusi ya fitar.

An kashe mutanen kauyen da dama tare da raunata wasu da dama sakamakon wani bam da aka harba na rundunar sojojin Najeriya.

Sanusi ya soki sojoji da fitar da bayanai masu karo da juna kan lamarin Tudun Biri.

“Bayani masu cin karo da juna da sojojin Najeriya suka bayar ya zuwa yanzu sun nuna rashin mutunta rayukan fararen hula tare da bayar da shawarar kokarin da hukumomi ke yi na boye wadannan munanan take hakkin dan Adam. Hare-haren jiragen sama da ke haifar da kisa ga fararen hula na zama na yau da kullun. Wannan sam ba za a amince da shi ba,” inji Sanusi

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp