Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce, wasu ‘yan fafutikar zaɓen 12 ga watan Yunin 1993 da aka soke, na sake haɗuwa domin yin amfani da halin da ake ciki na sauya fasalin kuɗin ƙasar wajen yi wa dimoradiyyar ƙasar ƙafar-ungulu.
Gwamnan ya ce waɗannan mutane na ɓoye ƙansu a matsayin jam’iyyun da ba sansu ba tare da yin aiki da ɗan takarar shugabancin babbar jam’iyyar adawar ta PDP, domin ƙaƙaba wa talakawa dokar amfani da sabbin takardun kuɗi.
Kalaman gamnan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke hukuncin hana Babban Bankin ƙasar CBN sake tsawaita wa’adin amfani da tsofin takardun kuɗin gdaga ranar 10 ga watan Fabrairu.
Karanta Wannan: Da gangan Emefiele ya bijiro da sauya kudi saboda borin kunya – Ganduje
A wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labaran jihar Muhammad Garba, ya fitar Ganduje ya zargi Babban Bankin ƙasar da masu goyon bayansa kan sauya fasalin takardun kuɗin ƙasar da kasancewa masu tsanani wajen ƙaƙaba wannan doka da za ta ‘wahalar’ da mutane.
Duk kuwa da kiraye-kirayen ‘yan ƙasar ciki har da majalisar dokokin ƙasar da ƙungiyar gamnoni.
Ganduje ya kuma yi zargin cewa goyon bayan da – babbar jam’iyyar adawa ta PDP tare da ɗan takararta na shugaban ƙasar Atiku Abubakar – suke bai wa CBN kan tsarin ya nuna akwai haɗin baki tsakaninsu domin yi wa dimokradiyyar ƙasar ƙafar-ungulu.