fidelitybank

Ana sa ran dawowar Tinubu bayan ya halarci ƙasashen China da Dubai har da Birtaniya

Date:

Ana sa ran shugaba Bola Tinubu zai dawo Abuja ranar Lahadi bayan ziyarar aiki da ya yi a kasar Sin da kuma ziyararsa a Burtaniya.

A ranar 29 ga watan Agusta, Tinubu ya bar Abuja zuwa birnin Beijing na kasar Sin, amma ya zarce a Dubai, UAE.

Ya isa birnin Beijing a ranar 1 ga watan Satumba domin fara ziyarar aiki a kasar Sin.

Shugaban ya fara ziyarar aiki a ranar 2 ga watan Satumba, inda ya gana da shugaba Xi Jinping a babban dakin taron jama’a.

An yiwa shugaba Tinubu gaisuwar bindigu 21. Ya kuma duba masu gadin.

Wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar ta ce, “An sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda biyar tsakanin Najeriya da China a wajen taron.

“Shugaba Tinubu ya jagoranci tawagarsa zuwa wani zagaye na tattaunawa da firaministan kasar Sin Li Qiang washegari.”

A yammacin wannan rana, shugaba Xi Jinping da uwargidansa Peng Liyuan, sun karbe shi a wajen liyafar maraba da nuna al’adun gargajiya a jajibirin taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC).

Tinubu ya bar birnin Beijing zuwa Landan, inda ya shafe kwanaki.

A ranar Alhamis, ya gana da Sarki Charles na uku don tattaunawa kan batutuwan da suka shafi sauyin yanayi.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp