Al’ummar kasar Angola sun fara kada kuri’a a babban zaben shugaban kasa wanda ake gani za a fafata sosai tun bayan da kasar ta samu ‘yanci a 1975.
A zaben shugaban kasar, za a fafata ne da shugaban da ke kan mulki João Lourenço da kuma wani da ya taba jagorantar kungiyar ‘yan tawaye ta Unita, Adalberto Costa Júnior.
Ana zargin jam’iyya mai mulkin kasar ta MPLA, wadda ke mulkin kasar fiye da shekaru 40, da rashin magance matsalar hahhawar farashin kayayyaki da talauci da kuma rashin aikinyi.
Shugaba Lourenco, dai ya yi alkawarin farfado da bangaren man kasar da kuma bunkasa tattalin arzikin, to amma rahotanni sun ce ba lalle masu kada kuri’ar su yar da dashi ba. In ji BBC.