A yau Laraba ne ake gudanar da bikin takutaha a jihar Kano wato ranar tunawa da suna kan haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.
Akasari dai a Najeriya ana bikin murnar zagayowar haihuwar annabi ne amma a Kano, su a ranar suna ake yin biki da taruka duk shekara.
Tun a farko dai, gwamnan jihar, Abba Yusuf ya ayyana yau, Laraba a matsayin ranar hutu
a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Baba Dantiye ya a Kano.
Dantiye ya ce gwamnan ya buƙaci jama’a da su yi amfani da wannan damar wajen yin tunani a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama tare da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.
Ya kuma buƙaci jama’a da su riƙa yin addu’a domin samun zaman lafiya da ci gaba a jihar musamman ma Najeriya baki daya.
“Muna addu’ar Allah ya ganar da mu cikin wannan mawuyacin lokaci kuma ya albarkace mu a wannan damina da kuma lokacin noman rani mai zuwa,” inji shi.
Akasari mutane musamman dalibai su kan yi jerin gwano a kan tituna inda suke rere waƙokin yabon annabi yayin da wasu kuma suke hawan dutse dala.