Ana fargabar cewa wasu mutane sun mutu a wani sabon rikici da ya ɓarke a garuruwan Omor da Anaku a ƙaramar hukumar Ayamelum ta jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.
Rahotonni na cewa mutum 10 ne ake zargin cewa sun mutu sakamakon rikicin da ya ɓarke ranar Litinin da yamma.
Karanta Wannan: ‘Yan sanda sun dakile harin da aka kai musu a Anambra
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Tochukwu Ikenga ya ce an kai ƙarin jami’an tsaro yankunan domin kiyaye rayuka da dukiyoyi al’umma.
Ya ƙara da cewa, kawo yanzu ba su san abinda ya janyo rikicin ba, to sai dai ya ce jami’ai na ci gaba da bincike domin daidaita al’amura. In ji BBC.