Ana fargabar cewa mutum 22 sun nitse a ruwa a wani hatsarin kwale-kwale a ƙauyen Kasabu da ke jihar Neja.
Mutanen dai na kan hanyarsu ta zuwa cin kasuwa a jihar Kebbi.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN, ya ruwaito darektan hukumar ba da agajin gaggawa na jihar, Salihu Garba, na cewa masu ninƙaya na can suna ci gaba da aikin ceto.
Ya ce babu wani fasinja da aka ceto zuwa yanzu.
Ya alaƙanta hatsarin jirgin ruwan da cika da kogin ya yi.
Hatsarin ya afku ne a ranar Litinin lokacin da ake tsaka da cin kasuwar Yauri.