Aƙalla mutum 20 ake fargabar sun mutu a wani hatsarin kwale-kwale da ya faru a kogin Andoni cikin ƙaramar hukumar Andoni ta jihar Rivers.
Wata sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar Andoni, Erastus Awortu ya fitar ce ta bayyana haka, har ma a ciki ya nuna kaɗuwarsa game da faruwar lamarin.
Mummunan hatsarin wanda ya faru ranar Talata da dare, an ce ya ritsa da kwale-kwalen fasinjoji guda biyu da ke kan hanyarsu ta zuwa Bonny.
Erastus Awortu ya bayyana ƙoƙarin ƙaramar hukumar tasa na ceto masu sauran kwana da kula da waɗanda suka ji raunuka da kuma gano gawawwakin mamatan da suka riga mu gidan gaskiya.
A Najeriya, hatsarin jirgin kwale-kwale, abu ne da ya zama ruwan dare musamman a yankunan da ke amfani da koguna wajen sufuri.