fidelitybank

Ana fargabar Daliban Jami’ar Nasarawa 3 sun mutu yayin karbar shinkafa

Date:

Daliban Jami’ar Jihar Nasarawa, NSUK, sun mutu ranar Juma’a a garin Keffi, sakamakon turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafin shinkafa da gwamnatin jihar ta yi musu.

Lamarin ya faru ne a dandalin taro inda aka ajiye buhunan shinkafa ana jiran isowar Gwamna Abdullahi Sule domin fara rabon kayayyakin.

A cewar wani dalibin da lamarin ya faru a gaban idonsa, Moses Ajah, ya ce gungun daliban da ke dakon shiga dandalin sun ci karfin jami’an tsaro tare da kutsawa ta kofar da lamarin ya faru.

Ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.

“Wasu daga cikin daliban sun yi ta kokawa da ‘yan sanda kan shinkafar, kuma da yawan daliban suka samu bayanai, lamarin ya lalace.

“A yayin da muke magana wasu daliban sun samu raunuka kuma suna karbar magani a makarantar,” NAN ta ruwaito yana cewa.

Ya ce wasu daliban ne suka dauko buhunan shinkafa suka garzaya dakunan kwanan dalibai da sauran wuraren zamansu duk da cewa gwamnan bai isa ba domin kaddamar da rabon.

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, an ga jami’an ‘yan sanda suna karbo kayan agaji daga daliban.

Da aka tuntubi Mista Abraham Ekpo, jami’in yada labarai da tsare-tsare na Jami’ar, ya ce yana sane da lamarin amma har yanzu bai samu cikakken bayani ba.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp